Skip to main content

Posts

WURIDIN NEMAN ARZIKI

Ga wanda ke neman arziki:  Ya yawaida karanta daya daga cikin addu'o'in nan idan kuma da hali ka karanta duka a kowace rana. Insha Allah, Allah SWT zai maka budi ta inda baka tunani. WURIDI NA FARKO: " Allahu Kafi, Allahu Ganiyyu, Allahu Fattahu, Allahu Jauwadu, Allahu Wadudu, Allahu Wasi'u, Allah Ladifu, Allahu Shahidu, Allahu Ni'imal Maula wa Ni'iman  Nasiru, Allahu yarziku man yasha'u bi gairi hisab" WURIDI NA BIYU: "Almalu walbanuna zinatul hayatud duniya, walba iyatus salihati khairun inda Rabbika thawaban wa khairun amala" Zakaja wuridin ayar nan ta sama sau dubu daya a kullum, tsawon kwana goma a kowane wata banda farkon watan Almuharram. WURIDI NA UKU: "Ka dawwama cikin karanta suratul Kahafi, Yasin, Izawaka da Tabaraka a kullum"

LADAN DA AKE SAMU KAFIN DA KUMA BAYAN SADUWA DA IYALI

An ruwaito cikin littafin "Shifa’us Sudur" cewa: Annabi S.A.W Yace; idan mace ta shiga cikin sha'anin hidimar mijinta ko tayi kwalliya domin neman yardar sa, ALLAH S.W.T zai rubuta mata lada guda goma kuma ya daukaka mata darajarta idan mijinta ya kirata tayimasa biyayya har ta dauki ciki zata kasance tanada ladan mai yin azumi da sallolin dare kullum a wajen daukaka kalmar ALLAH S.W.T wato jihadi. Sayyidatuna A'isha R.A Tace: hakika an baiwa mata alheri masu yawa to menene ku agareku maza? sai Annabi S.A.W Yayi murmushi Yace; "Babu wani mutum da ya riki hannun matarsa da nufin yin jima'i da ita sai ALLAH S.W.T Ya rubuta masa kyawawan ayyuka guda biyar idan yahada wuya da ita yanada lada guda goma idan ya sumbaceta yanada lada guda ashirin idan ya sadu da ita ALLAH S.W.T Zai bashi ladan da yafi duniya da abunda yake cikinta idan yatashi domin yin wankan janaba, ruwan wankan bai gudanaba a wani bangaren jikinsa sai an shafe zunubansa an kuma daukaka masa d

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI KASHI NA UKU

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI KASHI NA UKU 2 - Hukuncin idan matar da aka ari mahaifarta ta zamo kishiyar mai kwayoyin halitta: Mun bayyana cewa malaman Shari’ar Musulunci sun hadu akan haramci bayar da hayar mahaifa, idan mai mahaifar ba ta da dangantaka ta aure da namijin da aka hada maniyyin sa da kwayoyin halittar da aka ciro daga maniyyin matarsa.. Haka ma haramun ne a hada maniyyin namiji da kwayoyin halittar wata macen da ba matarsa ba; domin a shigar a cikin mahaifar matarsa.. Amma idan matar da za ta bayar da mahaifar tata kishiya ce ta mai kwayoyin halittar, ma’ana: matan mutum daya ne, mijinsu daya, to a nan malamai sun yi sabani; wasu suna ganin babu laifi a yi hakan saboda lalura, ganin cewa dukansu matan mutum daya ne. Wasu malaman kuma suna ganin cewa hakan haramun ne, domin ba shi da wani bambanci da surar farko da muka bayyana.. “al-Majma’ul Fiqhiy al-Islamiy”: wato Kungiyar masana ilimin Fiqhun Musulunci sun zartar da

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI KASHI NA BIYU

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI KASHI NA BIYU HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA” DA “SAYAR KO KYAUTAR DA MANIYYI KO KWAYOYIN HALITTA” Mun bayyana irin yanda wannan aiki na bayar da hayar mahaifa yake, da kuma yanda yanda ake sayar, ko kyautar da maniyyi, ko kwayoyin halitta a rubutun da ya gabata, inda muka bayyana surorinsu guda hudu, a yanzu -cikin ikon Allah- za mu hade wadanda suka yi kama da juna mu ambaci hukuncinsu kaman yanda malaman Shari’ar Musulunci suka bayyana.

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR DA KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA (MANIYYI) A MUSULUNCI KASHI NA DAYA

HUKUNCIN HAYAR MAHAIFA, DA SAYAR, KO KYAUTAR DA KWAYOYIN HALITTA A MUSULUNCI KASHI NA DAYA SHIMFIDA: Cigaban da aka samu –mai yawa- a fannin ilimin kimiyya da fasaha ya yi sanadiyyar sauyawan abubuwa masu yawa da aka sani a da, kaman yanda ya furzar da abubuwan da babu wanda ya taba tunanin cewa za su iya faruwa, wannan abu kuwa ya shafi fannonin: zamantakewa, da ilimin sadarwa, da kuma ilimin likitanci. A shekarun baya-bayan nan ne ilimin likitanci ya kawo wani gagarumin sauye - sauye a bangaren haihuwa, inda –a karon farko- duniya ta fara jin kalmomi irin su: “Hayar mahaifa” da “Bankin sayar da maniyyi” da “mahaifar kwalba” da “Istinsakh” (wato samar da jariri ba ta hanyar miniyyin namiji da mace ba) ko “colony” a Turance, da sauransu. Duk da cewa asalin wadannan abubuwa sun faru ne a kasashen da ba na Musulmi ba, sai dai cikin gaggawa suka tsallaka zuwa kasashen Musulmai, wasu kuma Musulman suka fara tsallakawa zuwa kasashen da ake yin wadannan ayyuka a asibitocinsu domin

HALACCIN YIN GWAJI (AWO) KAFIN AURE

Babu laifi a yi gwajin Genotype, ya ma inganta Manzon Allah SAW Ya yi umurni da abu makamancin haka, sannan idan ya bayyana akwai qaqqarfar yuyuwar haihuwan yara SS babu laifi a fasa wannan auren. ALLAH SWT Ne masani Amsa daga Dr Ibrahim Maqary Zaria

HUKUNCIN SIYAN KAYAN DA HUKUMAR CUSTOM TAYI GWANJO

Hukumar Custom tana yin gwanjo ne na kayan da ta kwace a hannun wadanda suka karya dokokin shiga da ficen kayayyaki kaman yarda doka ta tanadar Shi dai shige da fice na kayan da gwamnati ta hana ta barauniyar hanya yana cutar da tattalin arzikin kasa. Shi kuma cutar da tattalin arzikin kasa cutar da al'umma ne baki daya wanda kuma haram ne ka cutar da yan'uwanka.

KA KO SAN DA WANNAN A MUSULUNCI?

HADISI NA FARKO: MANZON ALLAH (S.A.W) ya na cewa Wanda ya karanta Qulhuwallahu Ahad kafa 10x ALLAH ya yi masa Alkawarin zai gina masa katafaren gida a gidan Aljanna. Sai Sayyidina Umar ya ce Ai to in haka ne sai mu dinga yawaitawa, sai MANZON ALLAH (S.A.W) ya ce ALLAH (S.W.T) shine mai yawaitawa ALLAH (S.W.T) shine mai tsabtacewa.  HADISI NA BIYU : MANZON ALLAH (S.A.W) ya na cewa duk wanda ya karanta suratul Kahfi a ranar juma'a ALLAH (S.W.T) zai cika masa hasken sa har zuwa wata juma'a mai zuwa yana cikin haske yana cikin farin ciki.

BANBANCI TSAKANIN MANIYYI, MAZIYYI, WADIYYI, DA KUMA HUKUNCE-HUKUNCEN SU

Wajibine kowani baligi ko baliga su san hukunce-hukuncen su domin gyara ibadunsu. HUKUNCIN FITAR MANIYYI shine: fitowar sa tana wajabta wankan janaba akan namiji ko mace. LAUNIN MANIYYIN NAMIJI: ruwane mai kauri fari wanda yake fitowa yayin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da zakari. Sannan yana tunkudo juna lokacin dayake fitowa, kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino, ko damammen gari, idan ya bushe yana kamshin kwai. LAUNIN MANIYYIN MACE: Ruwane tsinkakke, mai fatsi-fatsi, Wani lokacin kuma yana zuwa fari, wanda yake fitowa yayin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da farji. Sannan yana tunkudo juna lokacin da yake fitowa. Kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino ko damammen gari, idan ya bushe shima yana kamshin kwai. HUKUNCINFITAR MAZIYYI: hukuncin sa shine a wanke farji gaba daya, da kuma inda ya shafa, kuma a sake alwala. LAUNIN MAZIYYI: Ruwane tsinkakke da yake fitowa, yayin karamar sha'awa, kamar tunanin aure ko kuma tuna wacce kakeso, ko matark

MAGANIN MATSALOLI 7

Mutumin da yake cikin tsoro ya lazumci karanta: HASBUNALLAHU WA NI'IMAL WAKEEL. Mutumin da bakin ciki ya dame shi ya lazumci karanta: LA ILAHA ILLA ANTA SUB'HANAKA INNEE KUNTU MINAZ ZALIMEENA. Mutumin da masu makirci suka dame shi da makirci ya lazumci karanta: WA UFAWWIDHU AMREE ILAL LAAH. INNAL LAAHA BASEERUN BIL 'IBAADI. Mutumin da yake fama da wata jinya ko rashin lafiya, ya yawaita karanta: RABBI ANNEE MASSANIYADH DHURRU WA ANTA ARHAMUR RAHIMEENA.

HUKUNCIN YAWAN KOKONTO A CIKIN SALLAH

mai yawan shakku shine yayi kokari wajan yin sallah cikin jama'a wato tare da liman, Idan haka bata samuba sai ya lura da kokonton Nasa dadine ko ragi Idan ragine sai yazo da abunda ya rage sai yayi sujjada ba'adi, Idan karine sai yayi sujjada ba'adassalami shima. Kasani/kisani cewa mai mantuwa kashi Uku ne. 1- Wanda ya manta ko ya kara cikin wani Abu na farillah. Wannan dole sai yazo da Abunda ya rage Idan yakai matsayin farillah dole sai yacikoshi sai yayi sujja bayan sallama Idan ya bai tunaba har saida ya sallame Kuma Aka samu lokaci sallar ta baci sai ya sake Idan kuma ya tuna a kusa sai ya kawo Abunda ya rage yayi sujjada bayan sallama.

HUKUNCIN YIN JIMA'I DA AMARYA KO UWARGIDA TA DUBURA

Kamar yadda shari'a tayi hani akan aiwatar da jima'i ga uwargida ko amarya a lokacin da take haila, hakama jima'i ta dubura shari'a tayi hani mai tsanani akan aiwatar dashi. MANZON ALLAH (S.A.W) yayi hani ga wadannan munanan aiyuka (jima'i a lokacin haila da jima'i ta dubura) a Hadisai da dama. MANZON ALLAH  (S.A.W) yace: mutumin dake jima'i da matarsa ta dubura ALLAH Madaukakin Sarki ba zai dube shi da tausayi ba a ranar karshe. Shehun malami Imam Ghazzali (R.A) ya rubuta a cikin littafinsa "IHYA" cewa yin jima'i da mace ta dubura yafi laifi mai tsanani akan yin jima'i da ita yayin da take haila. (A sani dukkansu laifukane masu tsanani)

WANKAN JANABA (FARILLAI, SUNNONI DA MUSTAHABI) DA HUKUNCI A CIKIN WANKAN

FARILLAN WANKA: Yin niyya yayin farawa da gaggautawa da cuccudawa da gama jiki da ruwa. SUNNONIN WANKA: Wanke hannaye ya zuwa tsintsiyar hannu kamar yadda akeyi a alwala, da kurkure baki, da shaka ruwa, da fyacewa, da wanke kofar kunnuwa itace kofa mai shiga cikin kai, amman fatar kunne wajibine a wanke cikinta da bayanta. MU SAHABBAN WANKA: Farawa da wanke najasa, sannan a wanke azzakari inda a nan ne zaiyi niyyar wankan, sannan ya wanke gabban alwala sau dai-dai, sannan ya wanke saman jikinsa, da wanke kai sau uku da gabatar da tsagin jikinsa na dama, da karanta ruwa akan gabbai. HUKUNCE HUKUNCEN WANKA

RANAKU DA LOKUTTAN DA ANSO A GABATAR DA JIMA'I A CIKINSU

Ranaku da aka so ango ya gabatar da jima'i  da amaryarsa, domin fa'ida da samun falalarsu. Daren litinin, ana samun mahaddacin Alkur'ani. Daren talata, ana samun yaro/yarinya Shahidi. Daren alhamis, ana samu yaro/yarinya mai yawan tsoron ALLAH S.W.T, ko kuma wayayye mai kwarjini. Ranar juma'a kafin a tafi sallar Juma'a,  ana samun yaro/yarinya mai sa'a tare da samun kyakkyawan karshe. Jima'i a daren Juma'a na da matukar kyau domin shine mafi darajar darare guda bakwai. Annabi S.A.W yace:

JANABA TA KASU KASHI BIYU

na farko shine fitar maniyyi ta hanyar jin dadi na al'ada, a bacci ko a farke, ta hanyar jima'i ko waninsa. Na biyu shine buyan hashafa (wato kan azzakari) a cikin farji. Wanda yayi mafarki yana tarawa da mace amma maniyyi bai fito masa ba, to babu komai a kansa. Wanda ya samu busasshen maniyyi a jikin tufansa bai san yaushe ne ya same shi ba, to yayi wanka ya sake abunda ya sallata tun daga baccin sa na qarshe da yayi da wannan tufan.

NIYYAR GABATAR DA JIMA'I

GABATAR DA ADDU'O'I KAFIN JIMA'I Domin neman tsari daga shaidanu da kuma wasu illoli, anso lokacin da ango ke jima'i da amaryarsa ya karanta wannan addu'o'i,  ta wannan hanya ango da amarya zasu samu tsari. "Bismillahi Allahumma jannibnash shaidana wa jannibish shaidana ma razaktana" A lokacin da ango zai inzali (wato zai kawo maniyyi) zai karanta wannan addu'ar "Allahumma lataja alli shaidana fiimaa razaktana nasiiba." Wadannan  addu'o'i na da matukar Muhimmanci ga ango da amarya, don haka nake kira ga sabon ango yayi kokarin haddace wadannan addu'o'i kuma yayi kokarin koyawa amaryar in har bata iya ba.

ABUBUWAN DA AKA HARAMTA MARA ALWALA YI

Salla, tawafi, shafar Al-Qur'ani mai girma ko gafakarsa,bazai shafa da hannunsa ba ko da sanda da wanin wannan, sai dai juzu'in Al-Qur'ani wanda ake koyon karatu dashi, ba zai shafa allon da aka rubuta Alkur'ani mai qirma a cikinsa ba, ba tare da alwala ba, sai dai wanda yake koyon karatu a cikinsa ko mai koyarwa wanda zai gyarashi (wato allon). Yaro karami kamar babba yake a hukuncin daukar Alkur'ani ko shafa shi, zunubi yana kan wanda ya baiwa yaro Alkur'ani mai girma. Wanda duk yayi salla ba tare da alwala ba, da gangan yana sane da zama kafiri (in dai ya halatta yin hakan) ALLAH S.W.T  ya tsare mu ameen. Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

DAREN FARKO (ABUNDA YA KAMATA SABBIN MA'AURATA SUYI A SHARI'ANCE)

1. Nafarko su fara da gaisuwa irin wadda addinin muslunci ya tanadar mana (watau suyi wa junan su sallama). 2. Sai ango ya daura hannunsa a bisa goshin amaryarsa ya karanta wannan addu'ar: "Allahumma innee as'aluka min khairiha wa khairi maa jabaltaha 'alaihi wa'a uzhubika min sharriha wa sharri maa jabaltaha 'alaihi" ( Abu Dawud Ibn Maajah Al-Haakim Al-Bahaki da Abu ya'ala). 3. Daga nan sai ango da amarya su gabatar da Alwala sannan su gabatar da Sallah raka'a biyu bayan sun idar sai su karanta addu'o'i na neman 'ya'ya na gari.

ABUBUWAN DAKE WARWARE ALWALA

Abubuwan da suke warware alwala sune kari da sabanin kari. Kari shine: fitsari da gyangyadi da rihi da maziyyi da wadiyyi. Sabanin kari sune: bacci mai nauyi da suma da maye da hauka da sumbata da shafar mace idan anyi niyyar jin dadi ko an samu jin dadin da shafar azzakari da cin tafin hannu ko cin yatsu. Hukuncin kari. Wanda yayi kokwanto a cikin kari ya wajaba a kansa ya sake alwala, sai dai idan ya kasance mai yawan kokwanto ne to babu komai a kansa. Ya wajaba a kansa ya wanke azzakarinsa gaba daya idan mazziyi ya fito, amman bazai wanke maraina ba. Note: mazziyi ruwa ne mai fitowa yayin karamar sha'awa ta hanyar tunani ko kallo ko waninsa. Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

FASALI A CIKIN BAYANIN TSARKI (RABE-RABEN TSARKI)

TSARKI YA KASU KASHI BIYU: Tsarkin kari da tsarkin dauda, gaba dayansu ba sa inganta sai da ruwa mai tsarki mai tsarkakewa, shine wanda launinsa bai jirkita ba da basa haduwa da shi a bisa hali mafi yawa, kamar misalin narkakken mai da sandararren mai da romo gaba dayansu da shuni da sabulu da dauda da makamancinsu, babu laifi idan ya hadu da tulbaya da kasar kanwa da kasar gishiri da jar kasa da makamancinsu. FASALI: idan najasa ta ayyana (wato aka san wurin da take) sai a wanke wurinta, idan ta rikitar sai a wanke tufan gaba dayansa

FARILLAN ALWALA, SUNNONIN ALWALA, MUSTAHABBAN ALWALA DA KUMA YADDA AKE GYARA ALWALA

F arilla alwala: niyya da wanke fuska da wanke hannaye zuwa gwiwar hannu da shafar kai da wanke kafafuwa zuwa ido-sawu da cucudawa da gaggautawa. Sunnonin alwala: wanke hannaye izuwa tsintsiyar hannu yayin farawa, da kurkure baki, da shaka ruwa, da fyacewa, da dawo da shafar kai, da shafar kunnuwa, da sabunta ruwa dan shafar kunnuwa, da jeranta farillai.

YADDA AKEYIN SALLAR GAWA

Yanda Akeyin Sallar gawa daga Annabi (saw). Kamar yanda wasu daga cikin 'yan uwa  Suka nema cewa Ayiwa mutane Karin bayani Akan Sallar Jana'iza Muna Rokon Allah ya bamu dacewa cikin Abunda zamu fada. Da farko dai mutum Zai Qudurta Niyya a ransa. Idan Namiji ne mamacin Sai liman ya tsaya saitin kan sa, Idan Mace ce Sai liman ya tsaya tsakiyar ta daidai. Sai yayi kabbara ta farko, sai Fathi daya da sura cikin gajerun Surori ko wasu Ayoyi a takaice Sai ya sake Kabbara ta biyu, sai ya kawo Salati ga Annabi (saw) Salatu Ibrahimiyya. Sai yayi kabbara ta Uku, bayan kabbara ta Uku sai ya kawo wannan Adu'ar

SHARUDDAN TUBA

Yin nadama akan abinda ya wuce, da yin niyyar ba za a sake komawa kan sabon ba har abada. Kuma ya bar sabon nan-take idan ya kasance yana cikin aikin sabon ne. bai halatta a gare shi ba ya jinkirta tuba, bai halatta ba ya ce; in ALLAH ya shirye ni na tuba ba, fadar haka yana daga alamomin rashin arzikin lahira da tabewa da rashin basira.

FARKON ABINDA YAKE WAJABA AKAN BALAGAGGE

Ya iganta imaninsa sannan yasan abinda zai kyautata farillan aininsa da shi, kamar ilimin hukunce-hukuncen sallah da tsarki da azumi. Ya wajaba a kansa ya kiyaye iyakokin ALLAH tsarkakken Sarki tun baiyi azaba a gare shi ba. Ya wajaba a kansa ya kiyaye harshensa daga maganganu na sabo da munanan maganganu da duk wani zance mara dadi, ya kiyaye harshensa daga rantsuwa da sakuwar matsarsa, ya nisanci yin barazana ga musulmi da walakantashi, da zaginsa da tsorata shi ba tare da hakkin shari’a ba.

MAGANIN KARFIN MAZA KO MATA A MUSULUNCE

kala-kalar abincin dake samar da karfin maza/mata  (sperm), da kuma kuzari a jikin ango da amarya. HATSI: 1. Alkama ko kuma duk wani dangin abinci da ake samarwa daga gareta. 2. Shinkafa. 3. Wake. GANYE: 1. Albasa. 2. Galik. 3. Karas. 4. Dankali. 5. Kwakwa. 'YA' YAN ITATUWA: 1. Ayaba. 2. Mangoro.

ISTIMNA'I (masturbation) da HUKUNCIN SA

ISTIMNA'I ( masturbation) shine shine mutum ya rika wasa da al'aurassa har ya fitar da maniyyi, HUKUNCIN ISTIMNA'I Farko dai akwai hadisai wadanda suka nuna fushi na ubangiji akan mai aikata hakan, Hukuncinsa ga malaman mazhabobi guda hudu, Imam Malik Imam Shafi'i. Sun tafi akan haramta shi don haka a wurin su dole mutum yayi aure ko ya kame har zuwa lokacin da Allah zai bashi ikon yin aure.

ADDUAR DA MANZON ALLAH (SAWW) YAKE KARANTAWA IDAN ZAI KWANTA BARCI

ﺑِﺎﺳْﻤِﻚَ ﺭَﺑِّﻲ ﻭَﺿَﻌْﺖُ ﺟَﻨْﺒِﻲ، ﻭَﺑِﻚَ ﺃَﺭْﻓَﻌُﻪُ، ﻓَﺈِﻥْ ﺃَﻣْﺴَﻜْﺖَ ﻧَﻔْﺴِﻲ ﻓَﺎﺭْﺣَﻤْﻬَﺎ، ﻭَﺇِﻥْ ﺃَﺭْﺳَﻠْﺘَﻬَﺎ ﻓَﺎﺣْﻔَﻈْﻬَﺎ، ﺑِﻤَﺎ ﺗَﺤْﻔَﻆُ ﺑِﻪِ ﻋِﺒَﺎﺩَﻙَ ﺍﻟﺼَّﺎﻟِﺤِﻴﻦَ . Bismika Rabbee wadha'atu janbee , wa bika 'arfa'uhu, fa'in 'amsakta nafsee farhamhaa, wa 'in 'arsaltahaa fahfaz'haa, bimaa tahfazu bihi 'ibaadakas-saal iheen.

ISTIGFARIN DAYA FI KOWANE ISTIGFARI

Allahumma anta rabbi lailahailla anta kalaqtani, wa ana abduka wa ana ala ahadika wawa'adika mastada'atu auzubika min sharri maa sana'atu, abu'ulaka bi ni'imatika alaiya wa abu'ubizambi fagfirli fa innahu layagafiru zunuba illa anta. wanda duk ya fadeta da rana yana mai yakini da ita sai ya mutu a wannan yinin wannan yana daga ahlin aljanna. wanda ya karanta da dare shima da yakini akanta shima dan aljanna ne. Salati 10 ga Annabi S.A.W 

SALATUL ISTIHARA

MANZON ALLAH mai tsira da amincin ALLAH ya kasance yana sanar damu yanda ake istihara acikin kowane irin al'amurra da muka kasance, harma yake cewa 'duk lokacin da daya daga cikinku ya kasance mai himmatuwa ya zuwa wani aiki to sai yai sallah raka'a biyu (2) sannan sai yace  "ALLAHUMMA INNI ASTAKIRUKA BI ILMIKA WA'ASTAQADIRUKA BI QUDIRATIKA WA'AS'ALUKA MIN FADALUKAL AZIM FA INNAKA TAQDIRU WALA AQDIRU Fa AnTA taALAMU WALA A'ALAMU WA'ANTA ALLAMULGUYUB, ALLAHUMMA IN KUNTA TA'ALAMU ANNA HAZAL AMRA KHAIRUNLI FIDINI WA MA'ASHII WA'AQIBATU AMRI"  Ko kuma mutum yace

FAIDODIN SALATUN NABIYYI (SAWW)

Idan ka yawaita salati da tasleemi ga Manzon Allah (saww) zaka samu rabauta da fa'idodi Masu yawa Kamar haka: 1. Cika Umurnin Allah da yace: "Salluu 'alaihi wa sallimuu tasleeman". 2. Allah zai maka salatai guda 10 IRIN NASA (SWT). 3. Allah zai sa Mala'ikinsa ma suyi maka salati. 4. Zaka samu biyan bukatarka da gaggawa, domin kuwa Salatun Nabiyyi (saww) shine mabudin kofar samun karbuwar Addu'a.

Sayyiduna Abubakrin R.A

Sayyiduna Abubakrin bai fifici sauran Sahabbai da yawan Sallah ko yawan Azumi, ko yawan Ruwayar Hadisai ba. Sai dai ya Fificesu ne da Yawan Soyayyar Manzon Allah (S.A.W.W). Wannan Soyayyar ta sanya ba ya ganin komai agabansa sai Allah da Manzonsa (S.A.W.W). Kuma wannan Soyayyar ce ta sanyashi yake da saurin Gaskatawa da zarar wani Umurni ko hani ya sauka. Wannan Soyayyar ce ta sanya Allah ya zabeshi ya zama Khalifan farko daga cikin Khalifofin Masoyinsa (S.A.W.W). Haka nan shima Manzon Allah (S.A.W.W) yana mutukar Qaunar Sayyiduna Abubakar (R.A). Har Watarana Sayyiduna Amru bn Al-aas (R.A) ya tambayi Manzon Allah (S.A.W.W) Wanene Wanda kafiso acikin Mutane baki dayansu?" Sai yace masa "A'isha". Sai yace "Acikin Maza fa?" Sai yace "Abubakar ne". Mutane sukan fuskanci bacin rai sosai daga Manzon Allah (S.A.W.W) aduk lokacin da suka 'bata ran Sayyiduna Abubakrin. Wannan Qarfin Soyayyar ce ta sanya Sayyiduna Abubakrin yafi kowa Imani

Dr Maqary yakan ce

"Yanzu alumman musulmi sun zama in dai suna son mutum  ko don kungiyansu daya ko aqeeda ko Wani dalili dai ya hada su tohm baya laifi a  wurrinsu duk ko girman laifin da yayi Zaa nemi uzuri... Idan yana iskanci ace  jazba ne. Idan asharari ne ace sahibul haal ne... Idan kuwa baa son shi tohm Abu  kadan Zai fada ko da ba hakan ya nufa ba a juya mashi magana ayi tawili ace ai  Ga abunda yake nufi ... Kuma ayi ta yayatawa..." Rab Sitteer ya rajul

CETON ANNABI GASKIYA NE

Shine farkon wanda zai nemi ceto awajen Ubangijinsa, kuma shine farkon wanda  za'a bama damar yayi ceto 1. Da farko zai ceci dukkan halitta, albarkacin ceton nasa (S.A.W.W) ne ma Ubangiji zai saurari halitta harma ayi musu hisabi 2. Akarkashin cetonsa (S.A.W.W) ne Sauran Annabawa da Manzanni suma zasuyi ceto abisa al'ummominsu 3. Waliyyan Allah, Shahidai da sauran Muminai su ma zasuyi ceto akarkashin cetonsa (S.A.W.W) 4. Zai ceci Ma'abota tarin Zunubi daga cikin al'ummarsa (S.A.W.W), Sanna daga Qarshe zaije har cikin Jahannama ya rika fidda Mutane. Ba zai bar duk wani Musulmi ko Mumini ba, sai ya fidda dukkan wanda yake da Imani azuciyarsa koda Misalin Kwayar Zarrah ne Ya Allah Domin falalarka da Rahamarka, Don Girman Jamalar Zatinka ka sanyamu acikin wadanda zasu shiga Aljannah ba tare da hisabi ko Uqubah ba.

ANNABI MUHAMMAD RASULULLAH (S.A.W.W) yace:

"waye zai karbi wadannan kalmomi guda biyar |5| yayi aiki dasu kuma yakarantar da mai aiki dasu? Sai Abu-Huraira yace gani nan, sai Annabi Muhammadu (s.a.w) yakama Abu-Huraira ya kirga yatsu biyar sai yace: 1:-Kakiyayi haramu, zaka kasance mafi Ibadan mutane. 2:-Kayarda da abinda Allah yabaka, zaka kasance mafi wadatar mutane. 3:-Ka kyauta tawa makabcinka, zaka kasance mumini. 4:-Kasowa mutane abinda kasowa kanka, zaka kasance musulmi. 5:-Kada kayawaita dariya, lalle yawa dariya tana kashe zuciya.Allah ya kiyayemu baki daya.Ameen Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

An Tambayi Manzon Allah (saww) Akan abubuwan da zasu shigar da Mutumgidan Aljannah. Sai yace:

An Tambayi Manzon Allah (saww) Akan abubuwan da zasu shigar da Mutum gidan Aljannah. Sai yace: "TSORON ALLAH, DA KUMA KYAWAWAN 'DABI'U". Sannan aka tambayeshi akan abubuwan da zasu sanya Mutum shiga Wuta, Sai yace: "HARSHE DA KUMA AL-AURA". - Imam Tirmizy ne ya ruwaito hadisin. Wannan hadisin yana karantar damu Muhimmancin kyawawan Dabi'u da kuma sanya Tsoron Allah azuciya, Sannan mutum ya guji fadar duk abinda yazo bakinsa, kuma mutum ya kiyaye Sha'awarsa. Ya Allah ka tsaremu da Qarfin Ikonka ameen. Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

Sayyiduna Uthman bn Affaan (ra) yace

Mutumin da yasan Allah, sani NA HAQIQA, yana da wasu alamomi guda takwas (wadanda ake ganeshi dasu). 1 & 2. Zuciyarsa zata kasance cike da tsoron Azabar Allah, da kuma kwadayin rahamarsa. 3&4. Harshensa zai kasance ko yaushe cikin furta yabo ga Allah, da kuma bayyana gidiyarsa gareshi. 5&6. Idanuwansa zasu kasance ko yaushe cikin Jin kunyar Ubangijinsa, da kuma Zubda hawaye cikin tunaninsa. 7&8. Zai kasance cikin Burin rabuwa da duniya ako yaushe, da kuma neman yardar Ubangijinsa. Ya Allah ka azurtamu da wadannan Halayen. Fatiha da salati 10 ga SHUGABA S.A.W. 

DARAJOJI GUDA 10 GAME DA SAYYIDUNA UTHMAN BN AFFAN (rta)

DARAJOJI GUDA 10 GAME DA SAYYIDUNA UTHMAN BN AFFAN (rta) Kafin mutuwar Shahadarsa, Sayyiduna Uthman (ra) ya gaya ma ABU THAWR AL- FAHMIY cewa: "Ina Kyautata zato awajen Ubangijina saboda wasu abubuwa guda goma wadanda na sanyasu amatsayin amana tsakanina dashi. Abubuwan sune: 1. Nine mutum na hudu wajen shiga Musulunci. 2. Manzon Allah (saww) ya aura min 'Yarsa ta cikinsa. 3. Da ta mutu ya Qara aura min da 'Yar uwarta. 4. Tunda nake ban ta'ba rera waka ba. 5. Tunda nake ban ta'ba Tunanin aikata mugunta ba. 6. Tun daga ranar da nayi mubaya'a ga Manzon Allah (saww) da hannuna na dama, ban sake shafar al'aurata da wannan hannun ba.

SAYYIDUNA ALIYYU bn ABI TALIB (ra) yace

"Watarana Mun fita Gefen Garin Makkah tare da Manzon Allah (saww).  «Bayan Fat'hu Makkah». Amma babu wasu Duwatsu ko Bishiyoyi da muka wuce ta kusa dasu fache sai munji suna cewa: "ASSALAMU 'ALAIKA YA RASULALLAHI" «Aduba Sunanut Tirmidhy hadisi na 3,646» Allahu Akbar! Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

A MOST READ HADITH

Watarana Manzon Allah (saww) ya hau kan DUTSEN UHUDU tare da Sayyiduna Abubakar (ra) da Sayyiduna Umar (ra) da Sayyiduna Uthman (ra). Sai Dutsen ya fara girgiza. Sai Manzon Allah (saww) yace: "KA NUTSU YA UHUDU!! ANNABI NE AKANKA TARE DA SIDDIQI GUDA DAYA, DA KUMA SHAHIDAI GUDA BIYU". (Sahihul Bukhary Juz'i na 5 shafi na 24). Wannan hadisin ma yana ishara ne shima izuwa ga ILIMIN GAIBU irin wanda Allah ya sanar da Manzonsa (saww). Kunga acikin wannan hadisin Manzon Allah (saww) ya bada labarin cewa : ★ SAYYIDUNA ABUBAKRIN SIDDIQI NE. ★ SAYYIDUNA UMAR DA UTHMAN SHAHADA ZASUYI. ★ YANA MAGANA DA DUWATSU, KUMA SUNA JIN MAGANARSA (SAWW).

ZAMAN TAHIYA

Zaman Tahiya da karanta tahiya a sallah a takaice. Sallah tana kunshe da zaman tahiya guda biyu ga wanda ya samu cikakkar sallah tare da liman, Zaman tahiya da karanta tahiya sunna ne mai karfi a sallah. Tahiya ta farko a sallah: Ana takaituwa akan lafazin tahiya ne a zama na farko. Tahiya ta biyu a sallah: A zaman tahiya na biyu a sallah ana karawa akan lafazin tahiya da salati ga annabi da alayensa wanda imamu Malik ya tafi akan cewa kana iya takaituwa da salatin Annabi koda ba hada da alayensa ba kuma sallah tayi. Imam shafi'i kuma ya tafi akan cewa wajibine ka hada da alayensa. Sannan kuma akwai addu'o'in neman tsari da wuta da kuma Dujjal ga wanda Allah yaba ikon haddacesu. Sallama a sallah farali ne sannan zaman da zakayi na gwargwardon fitar lafazin sallamar shima farali ne. Ku kasance tare damu domin kawo muku Lafazin tahiya da salatin Annabi da kuma adduar da ake bayan salatin. Wallahu ta'ala a'alam. Salati 10 ga Ann

FASSARAR SALATUL FATIHI-DAGA MALAM JAMILU ABDULLAHI DUTSIN-MA

Allah kayi tsira ga sayyidina Annabi Mahammadu wanda ya bude abunda yake rufe ( Duniya ta kasance rufe da duhu manzon Allah yazo ya budeta da hasken musulunci) (Aljanna ta kasance rufe Annabi shine wanda zai budeta) ma'anar (الفاتح لما أغلق ) cikin sha'anin manzon yanada yawa na buga maka misali da 2. (والخاتم لما سبق) Wannan kuma ayar Qur'ani ce ta tabbatar masa da haka. A cikin fadin Allah. (ولكن رسول الله وخاتم النبيئين)   Ma'ana Annabawa sun gabace shi shine cika makon annabawa. ناصر الحق بالحق Shi mai taimakon gaskiya ne tare da karfin gaskiyarsa ba don komai ba sai don tabbatar da gaskiya. والهادي الي صراطك المستقيم. Shima wannan ayar qur'ani ce ina Allah yake fadin ce وإنك لتهدي الي صراط مستقيم Hakika kai mai shiryatarwa ne ya zuwa tafarki madaidaici وعلي ءاله Kayi wannan tsira ya Allah ga Ahlinsa Saw. حق قدره ومقداره العظيم Dai dai gwargwadon darajarsa da girmansa a wurinka ya ubangiji "Wadanda suka tafi akan cewa tafi duk wani salati

KADAN DAGA YADDA BILAL YAKE SON SHUGABA S.A.W

WANI LAMARI MAI GIRGIZA ZUCCIYAR MASOYAN ANNABI MUHAMMADU S.A.W YA FARU BAYAN WAFATINSA yayinda sayyiduna Bilal yaga damuwa da kadaicin rabuwa da babban masoyinmu ya tsananta gareshi madina ta zamemashi tamkar keji abu ya zamo ko kiransallah baya iyayi domin da ya kawo wurin "ASH HADU ANNA MUHAMMADURRASULULLAH" sai yaji muryarsa ta shake ta tsaya don kuka da kaunar annabi S.A.W gani yake kamar zai waiwaya yagansa . Da yaga abu yatsananta gareshi saiya nemi iznin khalifa sayyiduna Abubakar Assaddiq R.A don ya tashi ya koma kasar Sham ya zauna acan tareda wasu cikin sahabban manzon Allah. 

HADISI MAI BAN TSORO

Wannan kuwa shine Hadisin da Bukhari Da Muslim suka ruwaito cewa:  Manzon Allah S.A.W. Ya ce: "Mai ZINA ba ya yin ZINA a lokacin da yake yin ZINA A halin yana da IMANI, haka nan BARAWO ba yin sata a lokacin da yake SATA a halin yana Mumini, Haka kuma Mashayin GIYA ba zai sha GIYA ba a lokacin da yake shan GIYA a halin yana Mumini. Kuma mai kwace ba zai kwace kayan wani ba, kayan da Mutane za su daga ido su Kyale shi saboda mamakin taurin zuciyarsa a halin yana matsayin Mumini, Haka nan mai Satar ganima ba zai sace ganima ba a halin yana matsayin Mumini. Saboda haka ku yi hankali da kanku ku yi hankali da Kanku. Haka ya zo a cikin Littafin Almishkat' a Babin Alkaba'ir.

YADDA AKE WANKAN JANABA

Kamar yadda yazo daga sheikh DAN ALMAJIRI kano Da farko za'a fara gusar da najasa sannan sai a wanke alqalami sannan sai ayi niyya kamar haka:  "BISMILLAHI NAWAITU GUSLUL JANABATI FARRDUN RAFA'UL HADASUL AKHBAR." sannan a wanke kai sau ukku(3) a chachchakuda a yayin wanke kan sannan a koma a wanke gabban alwala sau dai dai(1) sannan sai a tsaga jiki ya zuwa kaso biyu(2) a wanke kowane kaso daga ciki, gaba ya zuwa gaba, daga sama zuwa qasa daga qarshe idan an gama sai kace:  "ALHAMDULILLAHILLAZI ZAHABA ANNIL'AZA WA'AFANI." ma'ana: godiya ta tabbata ga UBANGIJIN daya tafiyar mani da qazanta ya bani lafiya. ALLAH YASA MU DACE AMEEN. Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

NIYYAR WANKAN JANABA,HAIDA,NIFASI DANA JUMA'A

NIYYAR WANKAN JANABA "Bismillahi nawaitu guslul janabati farrdun raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN HAIDA "Bismillahi nawaitu guslul haidi farrdun raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN NIFASI (BIQI) "Bismillahi nawaitu guslul nifasi farrdu raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN JUMA'A "Bismillahi nawaitu guslul juma'ati wajibun" Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

MUKE JAWA KANMU

Kar Ka Yarda Wani Ya Rude Ka Da Cewa Wai Duk Fituntunun Da Muke Fuskan Ta wai Gwamnati Ce Ko Goodluck Ne Ko Wanene Ko Wanene A'a Ba Haka Bane Ga Yadda Abin Yake Wallahi Mun Saki Allah Ne !!! Mun Bar Umarnin Allah !!! Wallahi Malam Mun Saki Umarnin Allah Da MukaYi Alkawarin Dauka Ne Yau Idan Ka Duba wa'annan Abubuwan Da Zan Lissafo Sun Zama Ruwan Dare A Wajen Musulmai Amma Banda Muminai Ma'ana Muminai Basa Aikatawa Su 1. Zina 2. Madigo 3. Luwadi 4. Sata

KHUDUBAR ANNABI MUHAMMAD(S.A.W) TA RANAR TARA GA WATAN ZUL-HIJJAH

KHUDUBAR ANNABI MUHAMMAD SALLALLAHU ALAIHI WASALLAM WANDA YAYI A KHUDUBAR RANAR TARA GA WATAN ZUL - HIJJAH , SHEKARA TA GOMA DA HIJIRA A DUTSEN ARAFAT (RANAR ARFA KENAN). ANNABI (SAW)YA FARA DACEWA: “Ya ku mutane ku bani hankalinku, domin mai Yiwuwa bazan sake kasancewa da ku bayan wannan shekaran ba, saboda haka ku saurari abinda nake gaya maku da kyau, kuma (ku isar da abinda zan gaya maku) ga wadanda basa wannan wuri a yau. Ya ku mutane kamar yadda kuka riki wannan wata, (na hajji) da wannan rana (ta arfa) da kuma wannan gari (na Makka) da girma kuma abin tsarewa, to, haka kuma ku riki Ran Musulmi da kuma Dukiyoyinsu da girma abin kuma karewa, ku maida wa Mutane kayan da suka baku Amana. Kar ku cuci kowa, saboda kar wasu su cuce ku, ku tuna fa, hakika ALLAH zai yi sakayya akan ayukakanku, ALLAH (SWT) ya hana cin riba,(wato kudin ruwa) saboda haka, duk abin da aka kulla ta kudin ruwa sai a warware shi. Ku yi hattara da shaidan, domin kiyaye Addininku. Yanzu kan ya fidd

HADITH NA DAYA

Hadisi na farko daga littafi mai albarka na imamu Muhyiddin abu zakariyya, yahya dan sharafu annawawy Allah yai rahma agareshi madawwamiya. Ana kiran wannan littafi da Arba'inannawawy, saboda dan ganta sunan zuwa ga wanda yarubutashi(shine imamu annawawy) kuma nasabarsa(nawawy). Sannan malam Ahmad dan Abdurrahman dan rajab ya qara Hadisi takwas(8) daga cikin wannan littafi saboda haka suka zama hadisai hamsin kenan. Malamai dayawa sunyi sharhin wannan littafi, a cikinsu akwai sharhin Ahmad dan Abdurrahman dan Rajab a cikin littafinsa mabayyani mai suna(Jami'ul Uluumi Wal Hikami). Daga qarshe muna rokon Allah ya bamu ikon yin wannan aiki mai girma da muka dauko. ( HADISI NA FARKO ) An karbo wannan hadisi daga sarkin muminai , baban Hafsin Umar dan Kaddabi Allah ya qara yarda agareshi ameen . Yace ! naji MANZON ALLAH ( S.A.W ) yana cewa : Lallai dukkan ayyuka basu tabbata saida niyya , kuma yana ga dukkan kowane mutum abunda yai niyya , wan

TAFARKIN TSIRA

ANNABI (SAW) yana cewa: Idan lokacin (Kiyaamah) yakusa, ayyukan (Alkhairi) zasuyi karanci, ROWA zata YAWAITA, FITINTINU zasu YAWAITA, haka kuma Alharju zai YAWAITA. Sai sahabbai (RA) sukace Menene Alharju? Sai Annabi (SAW) yace: Kashe-kashe. (Bukhari ya ruwaito a 6552). Yaa Allah ka Kare mana IMANINMU, ka kubutar damu daga fitintinun zamani. Kasa mucika da imani.

LADUBBAN SALLAMA

1. Mustahabi ne idan anyi sallama a hada hannu. Annabi(saw) yace wanda suka hada hannu za'a gafar ta musu zunuban su. 2. Kuma anfi so mutum ya fara gaisawa da mutane daga hannun daman sa. 3. Bayan mutum zai bar cikin mutane zai sake yin sallama. Manzon Allah (saw) yace tafarkon ba tafi ta karshen ba, ma'ana ladan su iri dayane. 4. Wanda yake tafiya shi zai yiwa na zaune, wanda yake kan abin hawa yayi wa mai tafiya. Wanda ya fara yin sallama lokacin da aka hadu shi yafi samun falala. 5. Ko kasan mutum ko bakan sanshi ba za kayi masa sallama. 6. Namiji zai iya yiwa mace, mace ma zata iya yiwa namiji sai de a kyautata niya. 7. Amma masu cewa Salamu'alaikum wannan ba sallama bace hausane kawai, amma yazo acikin Alqur'ani za ka iya cewa Salamun'alaikum. Hukunce-hukuncesallama yana da yawa mutum ya duba AL-ADABUL MUFRAD na Imamul Bukhari don karin bayani Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

NIYYAR YANKAN LAYYAH DAGAGIDAN ANNABI (SAW)

ﻣﻦ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻟﻤﻦ ﺃﺭﺍﺩ ﺃﻥ ﻳﺬﺑﺢ ﺍﻷﺿﺤﻴﺔ yanadaga sunnar ma'aiki gawanda yake da niyyar yanka layyarsa, ﺃﻥ ﻳﻘﻮﻝﻋﻨﺪ ﺍﻟﺬﺑﺢ yafadi wannan kalmar lokacin da zaiyi yanka. ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ، ﻭﺍﻟﻠﻪ ﺃﻛﺒﺮ ، ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻫﺬﺍ ﻣﻨﻚ ﻭﻟﻚ ، ﻫﺬﺍ ﻋﻨﻲ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺗﻘﺒﻞ ﻣﻨﻲ ) IDAN KUMA WANI ZAKA YANKAWA SAI KACE

NIYYAR WAZIFA,ZIKIRIN JUMA'A,LAZIMIN SAFE DA YAMMA

NIYYAR LAZIMIN SAFE Allahumma inni nawaitu an ata qarraba ilaika bi qira'ati wurdissabahil lazimi fi darikatil tijjaniyati iktida'a bi sayyadi Ahmad Tijjani RTA ta'abudan lillah. NIYYAR LAZIMIN YAMMA Allahumma inni nawaitu an ata qarraba ilaika bi qira'ati wurdil masa'i allazimi fi darikatil tijjaniyati iktida'a bi sayyadi Ahmad Tijjani RTA ta'abudan lillah. NIYYAR WAZIFA Allahumma inni nawaitu an ata qarraba ilaika bi qira'atil wazifatil tijjaniyati iktida'a bi sayyidina Ahmad tijjani RTA ta'abudan lillah NIYYAR ZIKIRIN JUMA'AT Allahumma inni nawaitu an ata qarraba ilaika bi tilawati hailalati juma'ati allazimati fi darikatil tijjaniyati iktida'a bi sayyadi Ahmad Tijjani RTA ta'abudan lillah.

ADADIN LAZIMIN SAFE DA YAMMA

ADADIN LAZIMIN SAFE 1.Istigfari         100 2.Salatul fatihi     100 3.Hailalah         100 ADADIN LAZIMIN YAMMA 1.Istigfari       100 2.Salatul fatihi   100 3.Hailalah       100

FASSARAR JAUHARA A TAKAICE

Kashi na 1 Allah kayi tsira da Aminci a bisa ainihin rahamar Ubangiji, kuma wanda yake shine (ya'aqut) na gaskiya Shi ya'aqut wani ma'adanine wanda yafi dukkan ma'adanai tsada don haka aka kamantashi da manzon Allah don manzon Allah shine yafi komai tsada Duniya da Lahira Wannan tsadar itace ta zamanto matattarar dukkan ilimomi na zahiri da badini Kuma shine hasken duk wani abin halitta wanda yake daga Annabi Adam Kuma ma'abocin gaskiya wanda yake gaban dukkan kowa a fadar ubangiji Haske wanda ya hudo ko ya fito da ma'aunoni na ribobi wadanda suke cike da  rahamomi ga dukkan zukatan da suke cike da zikiri na waliyan Allah da bayi salihai Kuma haskene wanda dashine Allah ya haskakawa bayinsa suka gane hanya madaidaiciya dashi wanda yake tattare da dukkan girma na matsayi.

TARJAMAR JAUHARA DA HAUSA

Allahumma salli wa sallim ala ainirrahmatir rabbaniyati wal yaqutatul mutahaqqiqatul ha'idati bimarkazil fuhumi wal  ma'aniy wannuril akwanil mutakawwinatul adamiyyi sahibul haqqir rabbani albarqil asda'i bimuzunil arbahil mali'ati likulli muta arridin minal buhuri wal awani wannuri kalami'illazi mala'ata bihi kaunikal ha'ida bi amkinatil makani allahumma salli wa sallim ala ainil haqqillati tatajalla minha  urushul haqa'iqil ainil ma'arifi siradika Tamil asqam Allahumma salli wa sallim ala dal'atil haqqi bil haqqi kanzil  aazam ifada tuka minka ilaika ha'idatun nurul mudalsam sallahu alaihi wa ala alihi salatan tu'arrifuna Biha iyyahu.  - DAGA MALAM IBRAHIM ALIYU MAI DIWANI Salati 10 ga Annabi S.A.W