Skip to main content

Posts

Showing posts from January, 2017

KA KO SAN DA WANNAN A MUSULUNCI?

HADISI NA FARKO: MANZON ALLAH (S.A.W) ya na cewa Wanda ya karanta Qulhuwallahu Ahad kafa 10x ALLAH ya yi masa Alkawarin zai gina masa katafaren gida a gidan Aljanna. Sai Sayyidina Umar ya ce Ai to in haka ne sai mu dinga yawaitawa, sai MANZON ALLAH (S.A.W) ya ce ALLAH (S.W.T) shine mai yawaitawa ALLAH (S.W.T) shine mai tsabtacewa.  HADISI NA BIYU : MANZON ALLAH (S.A.W) ya na cewa duk wanda ya karanta suratul Kahfi a ranar juma'a ALLAH (S.W.T) zai cika masa hasken sa har zuwa wata juma'a mai zuwa yana cikin haske yana cikin farin ciki.