Skip to main content

HUKUNCIN SHAFA HANNU A FUSKA YAYIN KAMMALA ADDU'A

Akwai Hadisai da dama wayanda Abu Dawoud da Ibn Majah da Dabarani da wasunsu sun ruwaito cewa kada a mayar da hannu sai an shafa fuska amma Malaman Hadisi suna suka a cikin ilahirin wadannan hadisai.



Idan mutum ya shafa fuskarsa don aiki da wadancan hadisai koda yake suna da rauni ana masa fatar dacewa, idan kuma ya qi shafawa saboda rashin ingancin hadisan a ganinsa, shima ana masa fatar samun ladar taharrinsa.

- Dr. Ibrahim Ahmad Maqary Zaria
(Chief Imam National Mosque Abuja, Nigeria)

Comments