Skip to main content

FARKON ABINDA YAKE WAJABA AKAN BALAGAGGE

Ya iganta imaninsa sannan yasan abinda zai kyautata farillan aininsa da shi, kamar ilimin hukunce-hukuncen sallah da tsarki da azumi.
Ya wajaba a kansa ya kiyaye iyakokin ALLAH tsarkakken Sarki tun baiyi azaba a gare shi ba.
Ya wajaba a kansa ya kiyaye harshensa daga maganganu na sabo da munanan maganganu da duk wani zance mara dadi, ya kiyaye harshensa daga rantsuwa da sakuwar matsarsa, ya nisanci yin barazana ga musulmi da walakantashi, da zaginsa da tsorata shi ba tare da hakkin shari’a ba.
Ya wajaba a kansa ya kiyaye ganinsa daga kallon haramun, bai halatta ba a gare shi ya kalli musulmi da irin kallon da zai cuce shi, sai dai idan musulmin mai yawan sabo ne a fili, toh wannan ya zama dole ya kaurace masa.
Ya wajaba a kansa ya kiyaye dukkanin gabbansa iyakar ikonsa. Ya yi soyayya don ALLAH, ya yi kiyayya don ALLAH, ya yarda da mutum saboda ALLAH, ya yi fushi don ALLAH, ya rika yin umarni da kyawawan aiki, ya yi hani ga barin mummunan aiki.
Karya ta haramta a gare shi, da giba, da annamimanci, da girman kai da kaye, da riya, da jiyarwa, da hassada, da gaba, da ganin fifiko akan wani, da yafice, da zunde, da wasa, da izgili, da zina, da kallon mace ajnabiyya, da jin dadin firarta, da cin dukiyar mutane ba tare da dadin rai ba, da ci da sunan ceto ko da sunan addini, da jinkirta sallah ga barin lokutanta.
Bai halatta a gare shi ba yayi abota da fasiki, ko ya zauna da shi in dai bada lalura ba, kada ya nemi yardar halatta a cikin abinda zai sabawa ALLAH Mahalicci.
ALLAH mai tsarki da daukaka ya ce : ( ALLAH da MANZONSA su ne suka fi wajaba mutane su nemi yardarsu indai sun kasance masu imani ) Suratul-Tauba 621.
Mai tsira da amincin ALLAH ya ce: “babu biyayya ga wani abin halitta a cikin sabon mahalacci”
Bai halatta ba a gare shi ya yi wani aiki har sai ya san hukuncin ALLAH a cikinsa, (idan bai sani ba) ya tambayi malamai, ya yi koya da masu bin Sunnar ANNABI MUHAMMADU (S.A.W), wadanda suke shiryawa ga bin ALLAH TA’ALA, masu tsoratawa ga barin bin shaidan, kada ya yardarwa kansa irin abinda ababan fallasa suka yarda dashi, wadanda rayuwarsu ta tozarta a cikin bin wanin ALLAH TA’ALA, ya girman asarar irin wadannan mutane, ya tsawan kukansu ranar Alkiyama”.
Muna rokon ALLAH yayi mana mawafaka ga bin Sunnar ANNABINMU MACECINMU SHUGABANMU MUHAMMADU S.A.W.s

POPULAR POST

DAREN FARKO (ABUNDA YA KAMATA SABBIN MA'AURATA SUYI A SHARI'ANCE)

1. Nafarko su fara da gaisuwa irin wadda addinin muslunci ya tanadar mana (watau suyi wa junan su sallama). 2. Sai ango ya daura hannunsa a bisa goshin amaryarsa ya karanta wannan addu'ar: "Allahumma innee as'aluka min khairiha wa khairi maa jabaltaha 'alaihi wa'a uzhubika min sharriha wa sharri maa jabaltaha 'alaihi" ( Abu Dawud Ibn Maajah Al-Haakim Al-Bahaki da Abu ya'ala). 3. Daga nan sai ango da amarya su gabatar da Alwala sannan su gabatar da Sallah raka'a biyu bayan sun idar sai su karanta addu'o'i na neman 'ya'ya na gari.

MAGANIN KARFIN MAZA KO MATA A MUSULUNCE

kala-kalar abincin dake samar da karfin maza/mata  (sperm), da kuma kuzari a jikin ango da amarya. HATSI: 1. Alkama ko kuma duk wani dangin abinci da ake samarwa daga gareta. 2. Shinkafa. 3. Wake. GANYE: 1. Albasa. 2. Galik. 3. Karas. 4. Dankali. 5. Kwakwa. 'YA' YAN ITATUWA: 1. Ayaba. 2. Mangoro.

FARILLAN ALWALA, SUNNONIN ALWALA, MUSTAHABBAN ALWALA DA KUMA YADDA AKE GYARA ALWALA

F arilla alwala: niyya da wanke fuska da wanke hannaye zuwa gwiwar hannu da shafar kai da wanke kafafuwa zuwa ido-sawu da cucudawa da gaggautawa. Sunnonin alwala: wanke hannaye izuwa tsintsiyar hannu yayin farawa, da kurkure baki, da shaka ruwa, da fyacewa, da dawo da shafar kai, da shafar kunnuwa, da sabunta ruwa dan shafar kunnuwa, da jeranta farillai.

BANBANCI TSAKANIN MANIYYI, MAZIYYI, WADIYYI, DA KUMA HUKUNCE-HUKUNCEN SU

Wajibine kowani baligi ko baliga su san hukunce-hukuncen su domin gyara ibadunsu. HUKUNCIN FITAR MANIYYI shine: fitowar sa tana wajabta wankan janaba akan namiji ko mace. LAUNIN MANIYYIN NAMIJI: ruwane mai kauri fari wanda yake fitowa yayin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da zakari. Sannan yana tunkudo juna lokacin dayake fitowa, kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino, ko damammen gari, idan ya bushe yana kamshin kwai. LAUNIN MANIYYIN MACE: Ruwane tsinkakke, mai fatsi-fatsi, Wani lokacin kuma yana zuwa fari, wanda yake fitowa yayin babbar sha'awa kamar saduwa, ko wasa da farji. Sannan yana tunkudo juna lokacin da yake fitowa. Kuma warinsa yana kama da warin hudar dabino ko damammen gari, idan ya bushe shima yana kamshin kwai. HUKUNCINFITAR MAZIYYI: hukuncin sa shine a wanke farji gaba daya, da kuma inda ya shafa, kuma a sake alwala. LAUNIN MAZIYYI: Ruwane tsinkakke da yake fitowa, yayin karamar sha'awa, kamar tunanin aure ko kuma tuna wacce kakeso, ko matark

ISTIMNA'I (masturbation) da HUKUNCIN SA

ISTIMNA'I ( masturbation) shine shine mutum ya rika wasa da al'aurassa har ya fitar da maniyyi, HUKUNCIN ISTIMNA'I Farko dai akwai hadisai wadanda suka nuna fushi na ubangiji akan mai aikata hakan, Hukuncinsa ga malaman mazhabobi guda hudu, Imam Malik Imam Shafi'i. Sun tafi akan haramta shi don haka a wurin su dole mutum yayi aure ko ya kame har zuwa lokacin da Allah zai bashi ikon yin aure.

NIYYAR WANKAN JANABA,HAIDA,NIFASI DANA JUMA'A

NIYYAR WANKAN JANABA "Bismillahi nawaitu guslul janabati farrdun raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN HAIDA "Bismillahi nawaitu guslul haidi farrdun raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN NIFASI (BIQI) "Bismillahi nawaitu guslul nifasi farrdu raf'ul hadasil akhbari." NIYYAR WANKAN JUMA'A "Bismillahi nawaitu guslul juma'ati wajibun" Salati 10 ga Annabi Muhammadu S.A.W 

WURIDIN NEMAN ARZIKI

Ga wanda ke neman arziki:  Ya yawaida karanta daya daga cikin addu'o'in nan idan kuma da hali ka karanta duka a kowace rana. Insha Allah, Allah SWT zai maka budi ta inda baka tunani. WURIDI NA FARKO: " Allahu Kafi, Allahu Ganiyyu, Allahu Fattahu, Allahu Jauwadu, Allahu Wadudu, Allahu Wasi'u, Allah Ladifu, Allahu Shahidu, Allahu Ni'imal Maula wa Ni'iman  Nasiru, Allahu yarziku man yasha'u bi gairi hisab" WURIDI NA BIYU: "Almalu walbanuna zinatul hayatud duniya, walba iyatus salihati khairun inda Rabbika thawaban wa khairun amala" Zakaja wuridin ayar nan ta sama sau dubu daya a kullum, tsawon kwana goma a kowane wata banda farkon watan Almuharram. WURIDI NA UKU: "Ka dawwama cikin karanta suratul Kahafi, Yasin, Izawaka da Tabaraka a kullum"

ZAMAN TAHIYA

Zaman Tahiya da karanta tahiya a sallah a takaice. Sallah tana kunshe da zaman tahiya guda biyu ga wanda ya samu cikakkar sallah tare da liman, Zaman tahiya da karanta tahiya sunna ne mai karfi a sallah. Tahiya ta farko a sallah: Ana takaituwa akan lafazin tahiya ne a zama na farko. Tahiya ta biyu a sallah: A zaman tahiya na biyu a sallah ana karawa akan lafazin tahiya da salati ga annabi da alayensa wanda imamu Malik ya tafi akan cewa kana iya takaituwa da salatin Annabi koda ba hada da alayensa ba kuma sallah tayi. Imam shafi'i kuma ya tafi akan cewa wajibine ka hada da alayensa. Sannan kuma akwai addu'o'in neman tsari da wuta da kuma Dujjal ga wanda Allah yaba ikon haddacesu. Sallama a sallah farali ne sannan zaman da zakayi na gwargwardon fitar lafazin sallamar shima farali ne. Ku kasance tare damu domin kawo muku Lafazin tahiya da salatin Annabi da kuma adduar da ake bayan salatin. Wallahu ta'ala a'alam. Salati 10 ga Ann

TARJAMAR JAUHARA DA HAUSA

Allahumma salli wa sallim ala ainirrahmatir rabbaniyati wal yaqutatul mutahaqqiqatul ha'idati bimarkazil fuhumi wal  ma'aniy wannuril akwanil mutakawwinatul adamiyyi sahibul haqqir rabbani albarqil asda'i bimuzunil arbahil mali'ati likulli muta arridin minal buhuri wal awani wannuri kalami'illazi mala'ata bihi kaunikal ha'ida bi amkinatil makani allahumma salli wa sallim ala ainil haqqillati tatajalla minha  urushul haqa'iqil ainil ma'arifi siradika Tamil asqam Allahumma salli wa sallim ala dal'atil haqqi bil haqqi kanzil  aazam ifada tuka minka ilaika ha'idatun nurul mudalsam sallahu alaihi wa ala alihi salatan tu'arrifuna Biha iyyahu.  - DAGA MALAM IBRAHIM ALIYU MAI DIWANI Salati 10 ga Annabi S.A.W